Mutane 11 Sun Rasu, Anyi asarar Sama da Naira Miliyan 10 Sakamakon Gobara A Kano

Date:

Daga Zubaida A Ahmad

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce akalla mutane 11 ne suka rasa rayukansu da dukiyoyinsu na kimanin Naira miliyan sama da Naira Miliyan 10 sakamakon gobarar da ta afku a wasu sassan jihar a watan da ya gabata na Yuli.

Kadaura24 ta rawaito Saminu Yusuf Abdullahi Jami’in hulɗa da Jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa Daya fitar.

Sanarwar ta ce Hukumar a karkashin jagorancin Alhaji Hassan Ahmad Muhammmad a cikin watan da ya gabata na Yuli 2021, ta samu kiran gaggawa daga tashoshin kashe gobara har 27 da ke fadin jihar.

A cewar sanarwar, Hukumar ta karbi kiran wuta 32, da Kira na ceto 64, sai kiran Karya 21.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “An kiyasta kadarorin da gobarar ta lalata N10,500,000, An kiyasta kadarorin da aka tseratar N27,900,000, an rasa rayukan Mutane 11, tare da Ceto rayuka 107”.

A cikin sanarwar, Hukumar Kashe Gobara ta umarci jama’a da su rika kula da wuta don gujewa tashin gobara.

Ya kuma umarci jama’a da su rika bin dokokin Hanyoyin don gujewa hatsari tare da yin kira ga Iyayen yara da su Rika sanya ido kan ‘ya’yansu don Gudun Wasa a kududufi a unguwannin su.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...

Al’ummar Kano ku baiwa AA Zaura hadin Kai domin ya kawo karshen fadan Daba – Baba Yawale

Daga Halima Umar Dogo   Babban Hadimin AA Zaura Alhaji Baba...

Gwamnatin Kano ta magantu kan Hukuncin kotu na zaben kananan hukumomi

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Kano ta bayyana farin...