2023 : Ba zan Nemi kujerar Shugaban Kasa ko Mataimaki ba – Ganduje

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa a Shekara ta 2023 Bai gayawa kowa Zai nemi kujerar Shugaban Kasa ko Mataimakin Shugaban Kasar nan ba.

Kadaura24 ta rawaito Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne Yayin Wata Hira da yayi da Gidan Radio Nagarta dake jihar Kaduna a safiyar Larabar nan.

Ganduje yace bashi da wata niyya ta Neman Waɗancan kujeru kamar yadda Wasu ke yadawa cewa Yana neman kujerar Shugaban Kasa ko Mataimakin Shugaban Kasa.

” Sau tari Waɗanda Suka damu ko Suka nuna kwalamarsu wajen nema Wata kujera a Kasar nan basu Cika Samun Nasara ba” inji Ganduje

Yace shi burinsa ya kammala mulkin jihar Kano lami lafiya ya Sami Wanda Zai gajeshi Wanda Zai Mai da hankali wajen kawowa Kano cigaba dai-dai gwargwado.

“Zamu duk Mai yiwuwa wajen ganin mun Magance yan Matsalolin da muke dasu ta Hanyar masalaha tunda dama ita Siyasa ai masalahace, Kuma da yake ma ni ba talakamin karfe gareni ba ,ni talakamina na cike yake da soso ta yadda ko na taka Mutum ba Zai sanma na taka shi ba”. Inji Gwamna Ganduje

Idan Mai karatu Zai tuna yasha Jin ana cewa Ganduje Yana Neman Shugaban Kasa ko Mataimakin Shugaban Kasa Idan ya kammala wa’adin Mulkin Kano.

162 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...