Mutane 11 Sun Rasu, Anyi asarar Sama da Naira Miliyan 10 Sakamakon Gobara A Kano

Date:

Daga Zubaida A Ahmad

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce akalla mutane 11 ne suka rasa rayukansu da dukiyoyinsu na kimanin Naira miliyan sama da Naira Miliyan 10 sakamakon gobarar da ta afku a wasu sassan jihar a watan da ya gabata na Yuli.

Kadaura24 ta rawaito Saminu Yusuf Abdullahi Jami’in hulɗa da Jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa Daya fitar.

Sanarwar ta ce Hukumar a karkashin jagorancin Alhaji Hassan Ahmad Muhammmad a cikin watan da ya gabata na Yuli 2021, ta samu kiran gaggawa daga tashoshin kashe gobara har 27 da ke fadin jihar.

A cewar sanarwar, Hukumar ta karbi kiran wuta 32, da Kira na ceto 64, sai kiran Karya 21.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “An kiyasta kadarorin da gobarar ta lalata N10,500,000, An kiyasta kadarorin da aka tseratar N27,900,000, an rasa rayukan Mutane 11, tare da Ceto rayuka 107”.

A cikin sanarwar, Hukumar Kashe Gobara ta umarci jama’a da su rika kula da wuta don gujewa tashin gobara.

Ya kuma umarci jama’a da su rika bin dokokin Hanyoyin don gujewa hatsari tare da yin kira ga Iyayen yara da su Rika sanya ido kan ‘ya’yansu don Gudun Wasa a kududufi a unguwannin su.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da nuna tallan maganin Gargajiya a Fina-finai da yawo a tituna

A wani mataki na tabbatar da bin ka'idoji tare...

Da dumi-dumi: NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

  Jam’iyyar NNPP ta nemi afuwar Shugaban kasa Bola Tinubu...

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...