Zargin Rashawa: EFCC ta kama tsohon gwamnan Nasarawa Tanko Al-Makura da matarsa

Date:

Hukumar EFCC a Najeriya ta kama tsohon gwamnan Nasarawa kuma sanata a yanzu Umaru Tanko Al-Makura da matarsa kan rashawa.

Jaridar Premium Times a Najeriyar ta rawaito cewa yanzu haka ana riƙe da tsohon gwamnan da matarsa a ofishin EFCC da ke Abuja.

Jaridar ta ce duk da cewa babu wasu cikakkun bayanai, majiyoyi na tabbatar da cewa kamen na da alaƙa da rashawa da aka tafka a mulkin shekara 8 da ya yi na gwamna a Nasarawa.

Al-Makura ya jagoranci Nasarawa daga shekara ta 2011 zuwa 2019 kafin daga bisani ya tafi majalisa a matsayin Sanata mai wakiltar Nasarawa ta kudu.

68 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...