Osinbajo zai zo Kano Ranar 26 ga Wannan Wata

Date:

Daga Surayya Abdullahi Kabara

Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ce Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osinbajo Zai ziyarci jihar Kano domin Bude wasu aiyuka tare da kaddamar da Wasu aiyukan .

Gwamnan ya bayyana hakan ne Yayin taron Majalisar Zartarwar Jihar na Wannan makon Wanda ya gudana a Ranar Juma’ar nan.

Yace Mataimakin Shugaban Kasar Zai zo ne Ranar 26 ga Watannna da muke ciki domin Bude wasu muhimman aiyuka da Gwamnatin Kano ta gudanar.

Gwamna Ganduje yace Aiyukan da Farfesa Yemi Osinbajo Zai bude sun hadar da gadar Dangi dake kan titin Gidan zo sai Cibiyar koyar da sana’o’i ta Dangote, Sannan zai ziyarci Kasuwar Duniya da Tashar tsandaurin ta dala sai Asibitin cutar Daji da Sauran aiyuka da dama.

Gwamna Ganduje ya Mataimakin Shugaban Kasar Zai Kuma kaddar da Wasu aiyukan a nan Kano Wanda gwamnatin jihar Kano zata gudanar.

Gwamnan yace a Ranar Asabar din nan za’a bada sandar girma ga Mai Martaba Sarkin Rano Alhaji Muhd Kabir Inuwa Sakamakon Rasuwar Marigayi Sarkin Rano Alhaji Tafida Abubakar Ila Wanda ya rasu a bara.

74 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Amfani da al’ada a cikin fina-finan kannywood ne ya hana masa’antar ci gaba – Khadija Osi

Jaruma a masana'antar Kannywood Khadija Muhammad wacce aka fi...

Nasarar da Ɗaliban Kano suka Samu a NECO Kokari ne na Gwamnatin Ganduje – Sanusi Kiru

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi...

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...