DA ƊUMI-ƊUMI: Iya mazauna Saudiya ne kawai za su yi aikin Hajjin bana

Date:

Daga Abubakar Sadeeq

Ma’aikatar Harakokin Hajji da Ummara ta Saudi Arebiya ta bayyana cewa iya ƴan ƙasa da mazauna Saudiya ne kaɗai za su yi aikin Hajjin bana (2021).

Haramain ta rawaito cewa alhazai dubu sittin (60,000) ne kaɗai, da ƴan ƙasa da baƙi na ƙasashe daban-daban da ke zaune a Saudiyya ɗin, sannan suka yi allurar rigakafin korona karo na ɗaya ko biyu, za su yi aikin Hajjin na .

Wannan Sanarwar dai ta Kawo Karshen jiran da aka dde ana yi na za’ayi Aikin Hajjin ko ba za’a yi ba, Kuma samarwar ta nuna cewa ba Wani maniyaci da Zai shiga Kasar Saudiyya a bana domin gudanar da Aikin Hajjin bana.

Kadaura24 ta rawaito a Shekarar data gabata ma dai irin Wannan tsarin akai wajen gudanar da Aikin Hajji Saboda abun da ka Kira da Magance yaduwar Annobar cutar Corona.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...