Ba’a arziki da aikatau – Dr. Zahra’u Umar

Date:

Daga Ummukursum Murtala

Kwamishiniyar harkokin mata da walwalar al’umma ta jihar Kano Dr Zahra’u Muhd Umar ta Bukaci Iyaye su daina tura ‘ya’yansu aikatau domin yin hakan bashi da Wani alfanu ga yaran.

Kwamishiniyar ta bayyana hakan ne Cikin Wani sako da Jami’ar Hulda da jama’a ta Ma’aikatar Mata Bahijja Malam Kabara ta aikowa Jaridar Kadaura24.

Malama Zahra’u Muhd tace ba’a taba Samun Mara Ilimi ya taka wani Matsayi ba a tarihin Duniya.

“Duk Shugabanimu da Gwamnonin da sanatocinmu ba’a taba Samun Wanda yayi aikatau a cikinsu ba , Rayuwa sukai da abun da Allah ya horewa Iyayen su” Dr Zahra’u Muhd

Kwamishiniyar ta Bukaci Iyaye da su Rika tawakalli da halin da Allah ya Barsu a ciki, talauci ba uzuri bane da za’a hana yara Ilimi a turasu aikatau ba.

Yace buri da bukatu na karya ne suke sawa Iyaye suke tura ‘ya’yansu aikatau wai don su Sami abubuwan da zasu biyawa yaran bukatunsu na aure ko wani Abu.

Kwamishiniyar tac a Musulunci Haramun ne Iyaye laru da cewa ‘ya’yansu kanana Waɗanda basu balaga sune zasu dau dawainiyarsu ,tace kamata yayi Iyaye su dau dawainiyarsu’ya’yansu Haka addini yace “Inji Dr Zahra’u Muhd

270 COMMENTS

  1. — Джошуа: Усик вміє боксувати, він серйозний претендент // 05/09, 14:46 — Усик “засвітив” своїх спаринг-партнерів (ФОТО) // 05/09, 00:30 — Чемпіон wbo: Усик не зможе домінувати у суперважкій вазі // 03/09, 13:16 Энтони Джошуа Александр Усик смотреть онлайн Джошуа е с тегло 108,8 килограма, докато Усик е точно 100 килограма. Бокьорът е стопил голяма част от теглото си през последните месеци именно заради утрешния мач.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...