Adam A Zango ya sake komawa APC

Date:

Fitaccen jarumin fina-finan Hausa, Adam A. Zango ya koma bangaren jam’iyya mai mulki ta APC a Najeriya.

Jarumin na Kannywood da ke arewacin Najeriya, ya wallafa komen da ya yi ne a shafinsa na Instagram a ranar Talata inda aka gan shi tare da gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello.

“Kowa ya bar gida, gida ya bar shi.” Zango ya wallafa a shafinsa na Instagram dauke da hotuna da wani bidiyo da ya nuna shi tare da Gwamna Bello.

“Ga Adamu Zango a nan, muna maka barka da zuwa, ga shi sun dawo gida.” Gwamna Bello ya ce a cikin bidiyon mai tsawon dakika 29.

Gabanin zaben 2019, Zango ya sauya sheka ya koma babbar jam’iyyar adawa ta PDP, inda har ya gana da dan takarar shugaban kasar jam’iyyar Atiku Abubakar, ya kuma nuna magoya bayansa su zabe shi.

216 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abun da ya faru a Rano ba sai sake faruwa – Shugaban karamar hukumar ya tabbatar

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Shugaban karamar hukumar Rano malam muhd...

Bayan ganin wata Zulhijja, Saudiyya ta sanar da Ranar Arfat

Hukumomi a kasar saudiyya sun tabbatar da ganin jinjirin...

Kotu ta yanke hukuncin kisa ga matashin da ya kona masallata a Kano

Babbar Kotun Shari’a da ke Kano ta yanke hukuncin...

Sarkin Musulmi ya umarci yan Nigeria su fara duban watan Zulhijja

Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar...