Kano Pillars ta hau matsayi na daya bayan ta doke Enyimba

Date:

Zaharadeen saleh

Kungiyar kwallon kafa ta kano pillars ta hau matsayi na daya bayan data samu nasarar doke kungiyar Enyimba International daci biyu da daya, a cigaba da gasar cin kofin kwallon kafa ajin firimiya ta nigeria, a zagayen wasa mako na 25 da aka shiga a lahadin nan a kakar wasa ta 2020/2021.

Tunda farko dan wasa Enyimba ne mai suna Victor mboama ne ya jefa kwallo aragar kano pillars a mintina bakwai da fara wasan.

An kai kimani mintina 56 dan wasan kano pillars mai suna Rabi’u Ali ya rama kwallon ta hanyar bugun daga kai sai mai tsaran gida, a mintina 75 dan wasan kano pillars Ifeanyi ya kara kwallo ta biyu.

Yanzu haka bisa wannan nasara da kano pillars ta dawo matsayi na daya da maki 48, sai kungiyar Akwa united fc tana matsayi na biyu da maki 46 bayan data buga biyu da biyu da wikki Tourits a jihar bauchi.

Ga sakamakon ragowar wasanin da aka buga na mako na 25

Enugu Rangers 1 v MFM fc1
Kwara utd fc 3 v Jigawa G. Stars 0

Adamawa utd 0 v Plateau utd 2

Abia warriors 1 v fc Ifeanyi ubah 1

Dakkada fc 0 v Lobi stars 1

Heartland fc 2 v Rivers utd 2

Warri wolves 2 v sunshine 1

Katsina utd 2 v Nasarawa utd 1

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NAHCON ta sanar da ranar da za a fara jigilar Maniyatan Nigeria zuwa kasar Saudiyya

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar kula da aikin hajji ta...

Hisbah ta rushe wajen da aka ce sawun Ma’aiki ya fito a jihar Kano

    Hukumar Hisbah ta kai samame tare da rushe wani...

ƴan siyasa ne su ka kashe Arewacin Nigeria — Inji Gwamna Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa ‘yan...

Shugaban Karamar hukumar Bagwai ya kaddamar da aikn gada ta sama da Naira Miliyan 160

Daga Shu'aibu Sani Bagwai   Karamar hukumar Bagwai a jihar Kano...