NBC ta Bukaci Kafafen yada labarai a Nigeria Su Rufe Shafukansu na Twitter

Date:

Daga Ibrahim Sani

Gwamnatin tarayya ta Bukaci Dukkanin Kafafen yada labaran Radio da Talabijin a Kasar Nan dasu Rufe Shafinkansu na Twitter.


Hukumar kula da Kafafen yada labaran Radio da Talabijin ta Kasa ce ta bayyana hakan Cikin Wata sanarwa da Mai dauke da sa hannun Daraktan yada labaran Hukumar Farfesa Amstrong Idanchaba.


Sanarwar Hukumar tace ya Zama wajibi Kafafen yada labaran subi Umarnin da Gwamnatin tarayya ta Dauka na Dakar da Twitter a Nigeria.


NBC tace Rashin kishi ne Kafafen yada labaran Kasar nan su cigaba da amfani da dakatacciyar kafar ta Twitter wajen yada labarai ko Daukar labaran.


Tace Akwai dokokin Hukumar da suka baiwa Hukumar damar tabbatar da Wannan Mataki na gwamnatin Tarayya.


Idan za’a iya tunawa a kwanakin baya Kamfanin Twitter ya goge wani Rubutu da Shugaban Kasa Buhari yayi akan Tsagerun kudu Maso gabas Masu rajin kada Kasar Biafra.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...