NBC ta Bukaci Kafafen yada labarai a Nigeria Su Rufe Shafukansu na Twitter

Date:

Daga Ibrahim Sani

Gwamnatin tarayya ta Bukaci Dukkanin Kafafen yada labaran Radio da Talabijin a Kasar Nan dasu Rufe Shafinkansu na Twitter.


Hukumar kula da Kafafen yada labaran Radio da Talabijin ta Kasa ce ta bayyana hakan Cikin Wata sanarwa da Mai dauke da sa hannun Daraktan yada labaran Hukumar Farfesa Amstrong Idanchaba.


Sanarwar Hukumar tace ya Zama wajibi Kafafen yada labaran subi Umarnin da Gwamnatin tarayya ta Dauka na Dakar da Twitter a Nigeria.


NBC tace Rashin kishi ne Kafafen yada labaran Kasar nan su cigaba da amfani da dakatacciyar kafar ta Twitter wajen yada labarai ko Daukar labaran.


Tace Akwai dokokin Hukumar da suka baiwa Hukumar damar tabbatar da Wannan Mataki na gwamnatin Tarayya.


Idan za’a iya tunawa a kwanakin baya Kamfanin Twitter ya goge wani Rubutu da Shugaban Kasa Buhari yayi akan Tsagerun kudu Maso gabas Masu rajin kada Kasar Biafra.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...