Kungiyar kwallon kafa ta Enyimba ta fita daga gasar zakarun nahiyar afrika ta Caf .

Date:

Zaharadeen saleh

Kungiyar kwallon kafa ta Enyimba international dake garin aba, jihar abia ta fita daga gasar cin kofin kwallon kafa ta zakarun kungiyoyin nahiyar afrika ta caf confederation cup, a zagayen wasa na dab dana kusa dana karshe.

Kungiyar Enyimba fc ta fita daga gasar ne bayan data buga daya da daya da kungiyar Pyramid fc ta kasar masar a zagayen wasa na biyu da suka fafata a garin aba, bayan da a zagayen farko tayi rashin nasara daci hudu da daya a birnin cairo.

A yanzu kungiyar enyimba fc ta fita daga gasar confederation cup din ne da adadin kwallo biyar da biyu.

Kungiyar Enyimba fc itace kungiya daya tilo data rage a tsakanin kungiyoyi guda hudu suke wakiltar Nigeria a gasar zakarun nahiyar afrika.

Idan za’a iya tunawa tun a zagayen farko aka fitar da kungiyar kano pillars da plateau united ita kuwa kungiyar Rivers united a zagaye na kungiyoyi 32 aka fitar da ita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zaizayar kasa: Gwamna Abba gida-gida ya raba diyyar Naira Miliyan 600 A Kano

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Dalilin da ya hana Sarki Aminu Ado Bayero zuwa gidan yari na goron dutse a yau alhamis

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Rahotanni sun tabbatar da cewa Sarkin...

Matakai 3 da gwamnatin Kano ta dauka kan kafafen yada labarai a jihar

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnatin jihar Kano ta ce a...

Yadda manoma a Kano suka zargi jami’an Civil defense da karbar kudade a wajensu

Daga Umar Ibrahim kyarana   Manoman dajin dansoshiya dake karamar hukumar...