Kungiyar kwallon kafa ta Enyimba ta fita daga gasar zakarun nahiyar afrika ta Caf .

Date:

Zaharadeen saleh

Kungiyar kwallon kafa ta Enyimba international dake garin aba, jihar abia ta fita daga gasar cin kofin kwallon kafa ta zakarun kungiyoyin nahiyar afrika ta caf confederation cup, a zagayen wasa na dab dana kusa dana karshe.

Kungiyar Enyimba fc ta fita daga gasar ne bayan data buga daya da daya da kungiyar Pyramid fc ta kasar masar a zagayen wasa na biyu da suka fafata a garin aba, bayan da a zagayen farko tayi rashin nasara daci hudu da daya a birnin cairo.

A yanzu kungiyar enyimba fc ta fita daga gasar confederation cup din ne da adadin kwallo biyar da biyu.

Kungiyar Enyimba fc itace kungiya daya tilo data rage a tsakanin kungiyoyi guda hudu suke wakiltar Nigeria a gasar zakarun nahiyar afrika.

Idan za’a iya tunawa tun a zagayen farko aka fitar da kungiyar kano pillars da plateau united ita kuwa kungiyar Rivers united a zagaye na kungiyoyi 32 aka fitar da ita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sule Lamido, Ya Yi Barazanar Maka Shugabannin PDP a Kotu

  Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana...

Tsofaffin Kansiloli Sun Yi Saukar Alƙur’ani da Addu’a na Musamman ga Gwamna Abba

  Ƙungiyar tsofaffin kansiloli na jihar Kano ta gudanar da...

Hisbah ta kama mutane 25 bisa zargin shirya auren jinsi a Kano

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama akalla mutane...

Yadda ƴansanda suka kama wasu da suke zargin ƴanbindiga ne a Kano

Rundunar yansanda ta Kasa reshen jihar Kano ta ce...