Kungiyar kwallon kafa ta Enyimba ta fita daga gasar zakarun nahiyar afrika ta Caf .

Date:

Zaharadeen saleh

Kungiyar kwallon kafa ta Enyimba international dake garin aba, jihar abia ta fita daga gasar cin kofin kwallon kafa ta zakarun kungiyoyin nahiyar afrika ta caf confederation cup, a zagayen wasa na dab dana kusa dana karshe.

Kungiyar Enyimba fc ta fita daga gasar ne bayan data buga daya da daya da kungiyar Pyramid fc ta kasar masar a zagayen wasa na biyu da suka fafata a garin aba, bayan da a zagayen farko tayi rashin nasara daci hudu da daya a birnin cairo.

A yanzu kungiyar enyimba fc ta fita daga gasar confederation cup din ne da adadin kwallo biyar da biyu.

Kungiyar Enyimba fc itace kungiya daya tilo data rage a tsakanin kungiyoyi guda hudu suke wakiltar Nigeria a gasar zakarun nahiyar afrika.

Idan za’a iya tunawa tun a zagayen farko aka fitar da kungiyar kano pillars da plateau united ita kuwa kungiyar Rivers united a zagaye na kungiyoyi 32 aka fitar da ita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...