Fadan Daba: Yan Sanda sun Kama Matasa 30 a Kano Yayin Bikin Sallah

Date:

Daga Nafi’u Lawan Dan Salo


Yayin da aka kammala shagulgulan Bikin Sallah Karama Rundunar Yan Sanda ta Kasa reshen jihar Kano tayi holin Wasu Matasa Kimanin su 30 wadanda aka Kamo a wurare daban-daban bisa zarginsu da yin fadan Daba lokacin bukukuwan Sallah Karama.


Kadaura24 ta rawaito Mai Magana da yawun Rundunar Yan Sanda ta Kano DSP Abdullahi Haruna kiyawa ne ya bayyana hakan Cikin Wani faifen video Daya wallafa a Sahihin shafinsa na Facebook.


DSP Kiyawa yace Yan Sanda anti-Daba ne suka kamo matasan wadanda aka nuna hotunan su kowannensu Yana time da makamin da aka kamasu dasu a Yayin da suke tsaka da farma junansu.


Wasu daga Cikin Matasa da DSP Kiyawa ya zanta dasu sun tabbatar da cewa an kamo su ne Yayin da suke fadan Daba a yankunansu.


Kadaura24 ta rawaito Kakakin Rundunar Yan Sanda yace Kwamishinan Yan Sandan jihar Kano CP Sama’il Shu’aibu Dikko ya bada Umarnin dauke Matasan Daga ofishin anti Daba dake tal’udu zuwa Babban Sashin bincike na Rundunar dake Bompai domin gudanar da bincike tare da tura su kotu don girbar abin da suka shuka

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...