Kungiyar kwallon kafa ta Enyimba ta fita daga gasar zakarun nahiyar afrika ta Caf .

Date:

Zaharadeen saleh

Kungiyar kwallon kafa ta Enyimba international dake garin aba, jihar abia ta fita daga gasar cin kofin kwallon kafa ta zakarun kungiyoyin nahiyar afrika ta caf confederation cup, a zagayen wasa na dab dana kusa dana karshe.

Kungiyar Enyimba fc ta fita daga gasar ne bayan data buga daya da daya da kungiyar Pyramid fc ta kasar masar a zagayen wasa na biyu da suka fafata a garin aba, bayan da a zagayen farko tayi rashin nasara daci hudu da daya a birnin cairo.

A yanzu kungiyar enyimba fc ta fita daga gasar confederation cup din ne da adadin kwallo biyar da biyu.

Kungiyar Enyimba fc itace kungiya daya tilo data rage a tsakanin kungiyoyi guda hudu suke wakiltar Nigeria a gasar zakarun nahiyar afrika.

Idan za’a iya tunawa tun a zagayen farko aka fitar da kungiyar kano pillars da plateau united ita kuwa kungiyar Rivers united a zagaye na kungiyoyi 32 aka fitar da ita.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...