Ramadan : Rashin tsaro ne yasa kankana ta yi tsada a bana – Shugaban Kasuwar Na’ibawa

Date:

Daga Usman Kofar Mata

Kungiyar masu sana’ar sayar da kayan Marmari ta kasa reshen jihar Kano ta danganta tsadar da farashin Kankana tayi a wannan shekara da matsalar tsaro da jihohin da ake noman kankanar ke fuskanta.

Bayanin hakan ya fitone ta bakin jamiin hulda da jamaa na Babbar Kasuwar sayar da kayan marmari dake Naibawa Malam Murtala Yunusa yayin wata ganawa da wakilin Kadaura24  a wannan mako.

Murtala Yunus yace  “tabbas a bana an samu karancin kankana a wannan babbar kasuwar ta sayar da kayan marmari ta Naibawa, Dalilin tsadar kankanar kuwa shi ne gaskiya abana kusan  jihohin da sukafi yin  nomanta a nan Arewa abana ba suyi nomanta sosai ba saboda barazanar  tsaro da suke fuskanta, kamar jihar Zamfara da jihar Niger da garin Geidam da Damaturu da kuma wani bangare na jihar Sokoto”. Inji Malam Murtala

” A gaskiya wadannan  jihohi sune sukafi yin noman Kankana kuma sune suke cika wannan kasuwa da ita, amma abana saboda waccan dalili dana zayyana shine yasa basu yi nomanta ba kuma shine dalilin da yasa tayi karanci a kasuwar tunda babu ita” Inji Murtala Ayuba

“Sai dai ayanzu da muke wannan magana farashin Kankanar ya fadi kasa wanwar saboda yunkurin da karamar hukumar Bunkure ta nan jihar Kano tayi da kuma wasu kananan hukumomin jihar Jigawa na noma kankanar sosai tare da kawo ta wannan kasuwa, inda kamar yanda kake gani a yanzu kusan itace tafi kowanne kaya yawa a wannan kasuwa sabanin farkon kamawar watan Azumi da tayi matsanancin karanci a wannan Kasuwa” Inji Murtala.

Murtala ya kara da cewa abana musamman a farkon kamawar wannan  wata na  Azumin Ramadan farashin kankanar yayi tashin gwauran zabi inda ake saida  buhunta mai daukar kankana guda dari a ciki akan naira dubu dari da doriya (100,000)amma kuma a yanzu baya wuce naira dubu hamsin (50,000) a tsayayyan farashin kasuwa.

Ya lasafta farashin Abarba da Gwanda da Ayaba a matsayin kayayyakin da sukafi Kankana tsada a bana, amma acewarsa hankakin mutane yafi daukuwa akan tsadar Kankana saboda itace mafi bukatuwa ga mai Azumi kamar yanayi ke nunawa.

Kazalika ya bukaci manya da kananan yan kasuwa masu sarin kayayyaki a Kasuwar dasu sassauta farashin Kankanar kamar yadda farashin ta ya sauka a kasuwar da sauran kayayyakin bukatun yau da kullum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...