Yanzu-Yanzu: An kashe Dan ta’addan da ya shirya Sace Daliban Makarantar Kankara ta jihar Katsina

Date:

Rahotonni sun tabbatar da cewa fitaccen dan ta’addan da ya shirya sace ‘Yan Makarantar Kankara a cikin jihar Katsina, Auwalun Daudawa an kashe shi.
 Wannan na zuwa kwanaki kadan bayan ya koma daji.


 Kwamishanan tsaron harkokin cikin gida na jihar Zamfara, Abubakar Justice Dauran ne ya tabbatar wa DW Hausa da labarin.


 Daily Trust ta ruwaito cewa an kashe Daudawa ne da yammacin ranar Juma’a a lokacin da sukai musayar wuta da wasu gungun abokan hamayyarsu a dajin Dumburum da ke tsakanin karamar Hukumar Zurmi a Jihar Zamfara da karamar Hukumar Batsari a Jihar Katsina.


 Shahararren dan fashin nan ya yi kaurin suna bayan da ya kitsa kai hari a Makarantun Sakandaren Gwamnati da ke Kankara inda ya sace sama da ’yan makaranta 300 a cikin dare.
 Watanni biyu bayan haka, dan fashin ya bayyana a Gusau, babban birnin Zamfara, tare da mutanensa biyar inda ya sanar da tubansa tare da mika bindigogin AK guda 20 da wasu makamai ga ‘yan sanda.

2 COMMENTS

  1. Lallai Kadaura na bayar da gagarumar gudunmawa ga makaranta Hausa a Jafar sadarwa zamani.
    Allah ya taimaki Kadaura.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...