Alkalin Alkalai ya Amince da sake nada Alkalan kotun Shari’a 34 a Kano

Date:

Daga Abdulmajid Habib Isa Tukuntawa

Bayan samun nasarar cin jarabawa da kuma da cika duk wasu sharudda da Hukumar Kula da Shari’a ta gindaya Mai girma Babban Alkalin Alkalan Jihar Kano Nura Sagir Umar ya amince da nadin karin Alkalan Kotun Shari’a 34 a bangaren Shari’a na Jihar Kano.


Wannan na kunshe ne Cikin Wata sanarwa Mai dauke da sa hannun Mai Magana da yawun kotunan Jihar Kano Baba Jibo Ibrahim wadda kuma aka rabawa kaffefe yada labarai har da Kadaura24.


 Sanarwar ta ce Dukkanin sabbin Alkalan Kotun Shari’a da aka nada ana sa ran za a rantsar da su a ranar Juma’a, 25 ga watan Yuni, 2021 a dakin taro na Babbar Kotun Shari’a dake Kano da karfe 10: am

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...