Kaiyade kudade: sabon tsarin CBN karya Kasuwanci zai yi a Nigeria – Kungiyar Masu fataucin Shanu

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

 

 

Shugabancin kungiyar masu fataucin shanu da dabbobi ta kasa ya koka dangane da ka’idojin da babban bankin kasar nan ya samar na takaita yawan kudaden da za’a fitar a bankuna, da cewa hakan zai durkusar da kasuwancin yayanta a Nigeria.

 

 

Shugaban kungiyar Alhaji Mustafa Ali ne ya sanar da hakan a zantawarta da manema labarai a ofishinsa dake nan kano.

 

 

Mustafa Ali ya koka da cewar kamata yayi gwamnatin tarayya ta samar da tsarin da zai ceci yan kasuwa musamman kanana, kafin ta aiwatar da wannan sabon tsarin na sauya fasalin kudi ta yadda zai bunkasa tattalin arzikin kasuwanci a kasar nan.

Talla

 

Ya kuma koka dangane da yadda tsarin kasuwacinsu zai fuskanci kalubale idan har babban bankin kasa ya dage akan wadannan sabbin tsare-tsare da ya bijiro dasu na cewa mutum daya ba zai cire kudin daya haura naira dubu dari ba daga cikin asusun ajiyarsa na banki ba.

 

 

Shugaban ya bayyana cewa kasarnan ba ta kai munzalin da za tayi amfani da wannan sabon tsarin da ake yiwa lakabi da cashless policy ba, kasancewar tsarin tattalin arzikin kasar na cikin mashashshara.

 

 

Don haka ya yi kira ga gwamnatin tarayya kan ta gaggauta yin duba na tsanaki kan wannan sabon tsarin da ba zai haifar wa da kasar nan da mai ido ba, wanda idan gwamnati bata farga ba zai lalata kasuwancin dubunnan al’umma a fadin kasar nan.

 

 

Daga karshe ya yi kira ga ya’yan kungiyarsu da su cigaba da baiwa Shugabancin kungiyar hadin kai da goyon baya kasancewar kungiyar a shirye take wajen kare musu mutuncinsu, da kuma kwatar musu yancinsu musamman wadanda ke gudanar da kasuwacinsu a sassa daban-daban na jihohin kudancin Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...