Tsadar Abinci: Muhuyi Magaji ya gana da Masu shinkafa a Kano

Date:

A yau ne Shugaban hukumar Karbar korafe-korafe da hana ayyukan cin hanci da rashawa ta jahar Kano, Barrister Muhuyi Magaji Rimin Gado ya gana da Shugabancin kungiyar masu kamfanonin Sarrafa shinkafa ta kasa reshen jahar Kano, kan yadda za a magance matsalar tsadar shinkafar a jahar Kano.

A yayin zaman Barrister Muhuyi Magaji ya jagoran ta, Shugabancin kungiyar sun koka kan tashin gwauron zabi da dukkanin bangarorin kayan ayyukan su suka yi tare da neman hukumar ta shiga tsakani don samun rangwame daga gwamnatin tarayya.

A karshe Barrister Muhuyi ya basu tabbacin yin iya bakin kokarinsa domin ganin an saukaka wa Jama’a wahalar tsadar kayan abinci musamman ma shinkafa.

Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito yadda Kayan Abinchi sukai tashin gwauron zabi Musamman a yan kwanakinan.

63 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...