Kotu ta soke zaɓen fid da gwanin gwamna na APC a Taraba

Date:

Daga Ibrahim Ali Muhammad

 

 

Kotun tarayya da ke zamanta a Abuja babban birnin Najeriya ta soke zaɓen fitar da gwanin gwamna na jam’iyyar APC a jihar Taraba.

 

Alƙalin kotun mai shari’a Obiora Egwatu ya ce la’akari da hujjoji da shaidu da aka gabatar a gaban kotu, sun nuna cewa zaɓen fitar da gwanin da ka gudanar ranar 26 ga watan Mayun wannan shekara – wanda ya ayyana Sanata Emmanuel Bwacha a matsayin ɗan takarar – ba halastacce ba ne.

 

A watan da ya gabata ne dai wata kotun tarayya a birnin Jalingo ta soke zaɓen fitar da gwanin da jam’iyyar ta yi wa mista Bwacha, sakamakon ƙarar da ɗaya daga cikin ‘yan takarar ya shigar a gaban kotun yana ƙalubalantar sahihancin zaɓen.

Talla

 

Duka kotunan biyu a hukunce-hukuncen da suka yi sun bayar da umarnin ga uwar jam’iyyar da ta sake shirya wani sabon zaɓen fitarda gwani a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...