Sabon nau’in sauro mai sa zazzabi na kaura daga Asia zuwa Afirka

Date:

Daga Fa’iza Bala koki

Masana kimiyya sun ce wani mugun sauro da ke yada kwayar cutar da ke sa zazzabi, yana bazuwa zuwa Afirka daga Asiya, inda yake zama babbar barazana ga mazauna birni.

Wannan nau’in sauro wanda shi ne yake yada yawancin cutar maleriya da ake gani a biranen Indiya da Asiya, yana hayayyafa ne a cibiyoyin samar da ruwa na birane.
Kuma masanan sun ce wannan nau’i ne da kusan magungunan kashe sauro da ake amafani da su yanzu ba sa kashe shi.
Talla
BBC Hausa ta rawaito tuni wannan sauron ya sa an samu karuwar masu fama da cutar maleriya a Djibouti da Ethiopia, wanda hakan ya haifar da cikas ga yaki da cutar.
Masu bincike sun ce idan har ya ci gaba da yaduwa sosai a Afirka zai iya jefa rayuwar mutum miliyan 30 cikin hadari.
A nahiyar Afirka inda nan ne aka fi samun yawancin masu mutuwa a sanadiyyar cutar zazzabin sauro, galibi sauron da ke yada ta yana karkara ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...