Adam A Zango ya sake komawa APC

Date:

Fitaccen jarumin fina-finan Hausa, Adam A. Zango ya koma bangaren jam’iyya mai mulki ta APC a Najeriya.

Jarumin na Kannywood da ke arewacin Najeriya, ya wallafa komen da ya yi ne a shafinsa na Instagram a ranar Talata inda aka gan shi tare da gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello.

“Kowa ya bar gida, gida ya bar shi.” Zango ya wallafa a shafinsa na Instagram dauke da hotuna da wani bidiyo da ya nuna shi tare da Gwamna Bello.

“Ga Adamu Zango a nan, muna maka barka da zuwa, ga shi sun dawo gida.” Gwamna Bello ya ce a cikin bidiyon mai tsawon dakika 29.

Gabanin zaben 2019, Zango ya sauya sheka ya koma babbar jam’iyyar adawa ta PDP, inda har ya gana da dan takarar shugaban kasar jam’iyyar Atiku Abubakar, ya kuma nuna magoya bayansa su zabe shi.

216 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...