Adam A Zango ya sake komawa APC

Date:

Fitaccen jarumin fina-finan Hausa, Adam A. Zango ya koma bangaren jam’iyya mai mulki ta APC a Najeriya.

Jarumin na Kannywood da ke arewacin Najeriya, ya wallafa komen da ya yi ne a shafinsa na Instagram a ranar Talata inda aka gan shi tare da gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello.

“Kowa ya bar gida, gida ya bar shi.” Zango ya wallafa a shafinsa na Instagram dauke da hotuna da wani bidiyo da ya nuna shi tare da Gwamna Bello.

“Ga Adamu Zango a nan, muna maka barka da zuwa, ga shi sun dawo gida.” Gwamna Bello ya ce a cikin bidiyon mai tsawon dakika 29.

Gabanin zaben 2019, Zango ya sauya sheka ya koma babbar jam’iyyar adawa ta PDP, inda har ya gana da dan takarar shugaban kasar jam’iyyar Atiku Abubakar, ya kuma nuna magoya bayansa su zabe shi.

216 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Mun kama mutanen da mu ke zargi da kashe DPO Rano – Kiyawa

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta...

Ku Marawa Tinubu baya don ya ciyar da Kasar gaba – Faizu Alfiindiki ga yan Nigeria

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Jigo a jam’iyyar APC mai mulki,...

Maniyyaciya yar Najeriya ta maida dalar Amurka 5,000 da ta tsinta ga wani maniyyaci ɗan ƙasar Russia

    Wata maniyyaciya ƴar Najeriya mai suna Hajiya Zainab daga...

Gwamnatin Kano ta fara biyan tsofaffin kansilolin APC hakkokinsu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir...