Ganduje zai gabatar da kasafin kudin shekara ta 2023 wata mai kamawa ga majalisar dokokin Kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin jihar kano tace zata gabatar da kasafin kudin shekara ta 2023 ga Majalisar dokokin jihar kano a wata Mai kamawa na October.

 

Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan yayin taron majalisar zartarwa ta jihar kano wadda ake gabatarwa mako-mako a Gidan gwamnatin Kano.

 

Talla

Gwamnan Ganduje yace gwamnatin kano, tana kokarin taga tabi Sabuwar dokar kasafin kudi, wadda tace dole ne bangaren zartarwa ya gabatarwa majalisar dokoki kasafi kudi akan lokaci, Kuma ita ma majalisar ta kammala aikin ta akan lokaci domin fara aiwatar da sabon kasafin kudin a ranar daya ga watan sabuwar shekara.

Sashin wasu kwamishinoni

Yace ya kamata ma’aikatar kasafi da tsare-tsare ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin ta kammala Aikin ta akan lokaci, domin gwamnati ta gabatar da kasafin kudin shekara mai zuwa a watan gobe.

Sashin wasu kwamishinoni

 

Gwamna Ganduje ya kuma bukaci sabbin kwamishinonin da aka rantsar, wanda kuma suka fara halartar taron majalisar zartarwar a wannan makon, da su yi duk mai yiwuwa wajen ganin sun bada gudunmawa domin gwamnati ta kammala dukkanin aiyukan da ta ke gudanar a Kano kafin karewar Wa’adin gwamnati.

 

Ya kuma bukace su da yi aiki tukuru domin ganin jam’iyyar APC ta Sami nasara a zabukan shekara ta 2023 dake tafe

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...