Ambaliyar ruwa: Majalisar zartarwar kano ta Amince a rushe duk wani gini da aka yi shi a hanyar ruwa a kasuwar kwari

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Majalisar zartaswa ta jihar Kano ta amince tare da ba da umarnin yin alama tare da rushe duk wasu gine-ginen da aka gina a r Kwarin Gogau a cikin babban birni.

 

Kwamishinan yada labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya bayyana haka a lokacin da yake bayyanawa manema labarai sakamakon taron majalisar zartarwa na mako-mako, wanda aka gudanar a zauren majalisar zartarwa da ke gidan gwamnatin Kano.

 

 

 

Har ila yau, an bada umarnin rushe duk gine-ginen dake kan magudanun ruwa a ciki da kewayen Kasuwar Kantin Kwari da nufin kawar da duk wani abun da ke kawo cikas ga ruwan dake wucewa ta cikin kasuwar.

 

Bayan karbar rahotannin abubuwan da suka haifar da ambaliyar ruwa a kasuwar daga kwamishinnan ayyuka Engr. Idris Wada Saleh da na Muhalli, Dokta Kabiru Ibrahim Getso, majalisar ta kuma ba da umarnin a rushe duk wasu gine-gine na wucin gadi da aka a hanyar ruwa dake ciki da wajen kasuwar nan take.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...