Atiku zai zo Kano zawarcin Malam Ibrahim Shekarau zuwa PDP

Date:

Ɗan takarar shugabancin kasa a inuwar jam’iyyar PDP ta hamayya, Atiku Abubakar na shirin kai ziyara birnin Kano a gobe Lahadi domin karbar Sanata Ibrahim Shekarau a jam’iyyarsu.

 

Ziyarar ta Atiku da wani makusancinsa ya tabbatarwa BBC na zuwa ne adaidai lokacin da ake dakon jin matsayar Sanata Shekarau da tun a makon da ya gabata ake jita-jitar zai fice daga NNPP.

 

Kishi: Wata Mata ta Kashe Tsohon Mijinta a Jihar Kebbi

A farkon wannan makon mai ƙarewa tsohon gwamnan Kano kuma Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau, ya nuna alamonin raba gari da jam’iyyar NNPP.

 

Sanata Shekarau a wata hira da ya yi da BBC ya zargi jagoran jam’iyyar NNPP kuma ɗan takarar shugaban kasa, Rabi’u Musa Kwankwaso da yaudararsu.

Dole dan Kwangilar da ya Gina Gadar Lado ya Dawo ya gyara ta -Ministan aiyuka

Sannan ya shaida cewa suna kan tattauna da tuntubar juna domin sanar da matsayarsu kan ci gaba da zama a NNPP ko akasin haka.

 

Rundunar Sojin Nigeria ta Kori Sojojin da ake Zargi da Kisan Wani Malami a Yobe

Sai dai majiya mai karfi daga bangaren Atiku ta tabbatarwa da BBC cewa a gobe Lahadi Atiku zai gana da Shekarau a Kano a shirye-shiryen tabbatar da komawarsa PDP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...