Dole dan Kwangilar da ya Gina Gadar Lado ya Dawo ya gyara ta -Ministan aiyuka

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin tarayya ta bada umarnin nemo Dan kwangilar da yayi aikin gina gadar Ado Bayero, dake Gyadi Gyadi wadda akafi sani da Gadar Lado.

 

Idan za’a iya tunawa kusan kimanin wata guda kenan da lalacewar wani sashi na gadar, wanda hakan yayi sanadiyyar ba’a bin hannu daya wata hannun da zai kai ka Na’ibawa.

 

Karamin ministan ma’aikatar ayyuka da gidaje Hon. Umar Ibrahim El-yakub ne ya bayyana hakan yayin da yake duba yadda aikin titin kano zuwa Zaria ke gudana a yau asabar.

Kishi: Wata Mata ta Kashe Tsohon Mijinta a Jihar Kebbi

“Wannan gadar tana da matukar muhimmanci ga al’ummar jihar kano dama baki da suke Shigowa jihar don haka ya zama wajibi dan kwangilar da yayi aikin ya dawo domin gyara ta don al’umma su cigaba da mararta”. Inji El-Yakub

Talla
Talla

Minista yace tuni ya bada umarnin a nemo dan kwangilar da yayi aikin gadar saman Ado Bayero dake daura da Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano domin ya fara gyaranta.

” Cikin Wannan makon da Zamu shiga zaku ga anzi an gyara gadar sabods muhimmanci ta ga al’ummar jihar kano da Kuma harkokin sufuri da tattalin jihar kano da na kasa baki daya”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...