Wakar Asosa ta Ado Gwanja tasa wani Lauya zai maka hukumar Hisba a Kotu

Date:

  • Daga Buhari Ali Abdullahi

 

Wani lauyan Mai suna Barr. Badamasi Sulaiman Gandu yayi barazanar maka hukumar hisba ta jihar kano a gaban kotu matukar ta gaza dakatar da shahararren mawakin matan nan wato Ado Isa Gwanja daga fitar da wata Sabuwar waka da yayi Mai suan “Asoso”.

 

Da yake zantawa da wakilin Kadaura24 asafiyar yau Barista Badamasi Silaiman Gandu yace tuni ya aike da takardun gargadi na kwana uku ga hukumomin HISBA da hukumar Shari’a ta jihar kano domin su gaggauta dakatar da mawaki Ado gwanja daga fitar da sabuwar wakarsa mai suna “Asosa”.

 

Barr. Gandu Wanda ya zargi mawakin da yin amfani da kalaman da basu daceba acikin wakokinsa, yace barin irin wadannan wakokin a cikin al’umma zai kawo cikas wajen tarbiyyar yara masu tasowa.

 

Yanzu-Yanzu: Ganduje zai Samar da karin jami’o’i guda biyu a kano

Lauyan yace kamata ya yi gwamnatin jihar Kano ta dauki mawakin aiki a karkashin hukumar HISBA domin yin amfani da hikimarsa wajen fadakar da al’umma sabanin yadda yake amfani da hikimar ta wata hanya daban.

 

A karshe lauyan yayi barazanar maka hukumar HISBA agaban kotu matukar ta haura kwana uku bata dakatar da mawaki ado gwanjaba daga fitar da sabuwar wakar ba Mai suna “Asosa “

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...