Yanzu-Yanzu: Ganduje zai Samar da karin jami’o’i guda biyu a kano

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Gwamnati jihar kano ta yi alkawarin sake samar da jami’o’i guda 2 a Kano domin Kara bada damar inganta Ilimin matasa a jihar nan.

Kadaura24 ta rawaito Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabin yayin bude taron makon matasa wanda Majalisar dinkin duniya ta ware domin duba kan matsalolin matasa da Kuma lalubo hanyoyin da za’a magancesu, taron a gudanar da shi ne rufaffen dakin taro na filin wasa na Sani Abacha dake kofar mata.
Gwamna Ganduje yace tuni an tura sunayen kwalejin horar da malamai ta sa’adatu Rimi da Kuma kwalejin koyar da aikin noma ta Audu Bako dake Danbatta ga hukumar da take kula da jami’i ta kasa (NUC) domin neman sahalewa.
Yace yayi hakan ne domin Kara baiwa matasa damar su Kara karatu don inganta Rayuwar da Kuma cigaban jihar kano baki daya..
Idan wadannan jami’o’i suka tabbata Kano tana da jami’o’i guda 4 kenan mallakin gwamnatin jiha.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...