Abaya: Hukumar Hisba ta bayyana Matsayarta Dangane da Rigar Abaya

Date:

Daga Umar Ibrahim Sani Mainagge


Tun a kwanakin bayane wasu daga cikin matasa a jihar kano, suka dauki wata dabi’a tayin dan Kira ga duk budurwar data Sanya rigar abaya, hakan ta tilastawa ‘yan matan janye aniyarsu tayin yayin wannan Riga ta abaya a bikin Sallah karama data gabata.

Ko shakka babu wanana sara na ciwa ‘yan matan tuwo a kwarya tare da sakasu a cikin damuwa, Kuma haka ta tilastawa musu jibge wadannan riguna a gidajensu domin gujewa fadawa tarkon samarin kaga kenan abaya tazamewa ‘yan matan Dan zani Mai wuyar daurawa.

To sai dai Kuma a Wasu na cewa wannan Sara da samarin suka runguma hannu biyu-biyu tafara ciwa Hukumomi tuwo a kwarya, Hukumar nan mai hani da mummuna da Kuma umarnin da kyakkyawa wato Hukumar Hisba tafitar da matsayarta aka wannan sara tayin tozarci ga Yan Mata.


Ustaz Harun Muhammad sani ibni Sina shine babban kwamandan hisba na jihar kano yayi Kira ga samarin da su janye wannan aniyarsu tayin dan Kira ga ‘yan matan da suka sa rigar abaya domin kuwa riga da bata sabawa musulunci ba.

Sheikh Ibn Sina ya kuma Jan hankalin samarin dasu guji cin zarafin matune domin yin hakan ya sabawa addini Kuma ya sabawa Mutuntaka ta Dan adam .

Yace Hukumar su bazata lamunci Wannan mummunar dabi’ar ba , ya kuma bada tabbacin Hukumar zata saka Wanda guda da Duk Wanda aka Kama yaci zarafin Wata ‘ya mace data Sanya Abaya.

73 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...