Zabin Musulmi da Kirista a baya bai amfanawa Yan Nigeria komai ba – Oshomole

Date:

Tsohon Gwamnan Jihar Edo, Adams Oshiomhole, ya kare zabin Musulmai biyu a matsayin ’yan takarar jam’iyyar, inda ya ce a baya zabin Musulmi da Kirista bai tsainana wa Najeriya komai ba.

Ya ce lokaci ya yi da Najeriya za ta yi watsi da banbancin addini, kabilanci da na yanki, ta koma duba cancanta da kwarewa don kai ta tudun mun-tsira.

Da yake tattaunawa da gidan talabijin na TVC ranar Alhamis, Oshiomhole, wanda kuma tsohon Shugaban jam’iyyar APC na kasa ne, ya yaba da zabin Musulmai biyu a matsayin ’yan takarar, inda ya ce Tinubu ya yi abin da ya dace.

A makon da ya gabata ne dan takarar Shugaban Kasa na APC, Bola Ahmed Tinubu ya ayyana sunan tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Kashim Shettima a matsayin Mataimakinsa a takarar a zaben na 2023.

A cewar Oshiomhole, “Duk lokacin da jam’iyyun hamayya suka fara magana a kan zabin Musulmai biyu, a lokacin nake dada gamsuwa cewa matakin Tinubu a kan daidai yake.

Ya kuma ce ya gamsu da zabin Sanata Shettima saboda kwarewarsa da kuma tarihin abubuwan da ya aiwatar a baya.

Dangane da batun zargin da ake yi cewa Tinubu da Mataimakin nasa za su ‘Musuluntar’ da Najeriya, ya ce bai ga ta yadda za a yi Tinubun da ya gaza Musuluntar da iyalansa zai yi nasarar yin haka a Najeriya ba.

“Meye abin tsoro a wannan fargabar da wasu suke yi? Sun ce akwai barazanar za su Musuluntar da Najeriya. Shi kansa dan takarar (Tinubu), ya Musuluntar da iyalansa ne? Matarsa fa Kirista ce kuma Fasto?” inji Oshiomhole.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...