Ganduje Zai Samar da Cibiyoyin Adana Madarar Shano guda 200 a fadin jihar Kano

Date:

Daga Muhd Sale Hotoro


 Shirin bunkasa kiwo na makiyaya na jihar Kano, KSADP, ya ba da kwangila don tsarawa da kulawa da ayyukan tuntuba don kafawa da kula da cibiyoyin tattara madara har 200 a fadin kananan hukumomin 44 na jihar.  


Kadaura24 ta rawaito an ba da kwangilar ne ga kamfanin Messrs Teamwork Global Associates, wani kamfani na Yan  asali Jihar nan.


 Haka kuma, Shirin ya sanya hannu kan kwangilar tsarawa da kula da tuntuba don gina dakin gwaje-gwaje na likitocin dabbobi a Kundila, karamar hukumar Tarauni.  An bayar da wannan Aiki ga Kamfanin Kul-Dwell Consultants Ltd.


Jami’in yada labaran Shirin Ameen K. Yassar yace Kwangilolin za su hada da ayyukan Masu bada shawarwari, samar da ma’aikata bada horo da samar da taswirar da Samar da wurare daban-daban da ake son samarwa, da dai sauransu.


 Jami’an ba da shawarar za su ba da shawarar yadda za’a aiwatarwa da ayyukan dai-dai da sharuɗɗan da aka amince da su yayin yarjejeniyar.


 Da yake jawabi jim kadan bayan sanya hannu kan kwangilar, Babban Jami’in Gudanar da Shirin na Jihar Ibrahim Garba Muhammad ya ce: “Ainihin, wannan Shirin yana da niyyar gabatar da sabbin dabaru a cikin Aikin Samar da madara a jihar Kano da Kuma yadda za’a inganta tsarin ta Hanyar fasahar zamani”.


 A sakamakon haka, “KSADP na shirin gina cibiyoyin tattara madara tare da kayan aiki na zamani, tare da samar da Na’urar sanyaya madarari wanda zai haifar da karuwar bukatar kayayyakin kiwo, karuwar farashin madarar da, magance Matsaloli da batutuwan ingantar madara da Kuma  tsaftaceta”, Ibrahim Garba ya jaddada.


Babban Jami’in kula da Shirin ya ce dakin gwaje-gwajen kiwon lafiyar dabbobi yana daya daga cikin shirye-shirye da dama da aka gabatar da nufin bunkasa lafiyar dabbobi, da tabbatar da lafiyar abincin da dabbobin ke samu da kuma kiyaye lafiyar jama’a gaba daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...