Da dumi-dumi : Za mu iya hukunta Tinubu Kan kalamansa ga Shugaba Buhari – Abdullahi Adamu

Date:

Daga Halima Musa Abubakar
 Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya ce jam’iyyar zata iya hukunta Asiwaju Bola Tinubu, jigo a jam’iyyar na kasa, kan kalaman da ya yi akan shugaban kasa Muhammadu Buhari.
 A lokacin da ya ziyarci Abeokuta, babban birnin jihar Ogun, a ranar Laraba, Tinubu ya shaida wa wakilan jam’iyyar APC cewa ba dan shi ba, da Buhari bai za zama shugaban kasa ba.
 Ya ce bayan Buhari ya fadi zabe sau uku, Buhari ya yi kuka ya ce ba zai kara tsayawa takara ba, amma shi (Tinubu) yace ya je Kaduna ya roki Buhari ya sake tsayawa takara kuma zai yi nasara saboda da zasu mara Masa baya.
 Wannan tsokaci dai ya janyo cece-kuce a fadin kasar nan, inda da dama ke zargin Tinubu da kamanta kansa da Allah.
 Da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar jam’iyyar APC da ke Abuja ranar Asabar, Adamu ya ce, “Muna iya hukunta shi (Tinubu) kan kalaman da ya yi akan Shugaban kasa.
 Adamu ya kuma ce babu wani dan takarar shugaban kasa da aka haramtawa tsayawa takara a zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar da ake shirin yi ranar Litinin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...