Gobara ta kashe uwa da ɗanta a Kano

Date:

 

A jiya Alhamis ne wani ibtila’i , ya faru a unguwar Gandun Albasa, a layin Bala Burodo a birnin Kano, inda wata uwa mai suna Maryam Nura mai shekaru 35 da ɗanta ɗan shekara uku suka mutu sakamakon gobara da ta ƙone ginin da suke zaune a ciki. .

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Saminu Abdullahi ya fitar a yau Juma’a a Kano.

Abdullahi ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a jiya Da daddare.

“Mun samu kiran gaggawa da misalin karfe 2:07 na safe daga wani Ibrahim Ashiru kuma nan take muka aika da tawagarmu zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 2:11 na safe,” inji shi.

Ya ce “Ginin, gida ne mai dakuna biyar mai tsayin taku 75ft da 75ft, kuma gobarar ta rushe shi gaba daya.”

Daily Nigeria ta rawaito Abdullahi ya ce, an ceto wadanda lamarin ya rutsa da su ne a sume kuma aka mika su ga Insfekta Shehu Lawan na ofishin ‘yan sanda na Ƙwalli, inda suka garzaya da su asibitin kwararru na Murtala Muhammad, inda a nan ne kuma likitoci suka tabbatar da mutuwarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...