Kamata yayi ‘yan jaridu su maida hankali kan harkokin kiwo Lafiya don magance Matsalar da ake fama da ita – Dr. Rukayya Aliyu

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Wata malama a sashin koyar da aikin jarida dake Jami’ar Bayero Kano Dr. Rukayya Aliyu ta bukaci yan jaridu da su mayar da hankali kan rahoton daya shafi bangaren lafiya da sauran batutuwa da suke faruwa a yankunan karkara, dama batutuwan dake ci musu tuwo a kwarya,da nufin daga martaba kiwon lafiyar al’umma.

Dr Rukayya Aliyu ta bayyana hakan ne yayin wani taron karawa juna sani da kamfanin jaridar Solacebase ya shirya ga wasu yan jaridu hadin gwiwa da cibiyar binciken kwa-kwaf ta Wole Soyinka, da kuma gudauniyar MacArthur suka shirya, da nufin basu horo kan binciken kwa-kwaf musamman bangaren kiwon lafiya wanda aka gudanar a kano.

 

Kadaura24 ta rawaito Dr. Rukayya ta kara da cewa yan jarida suna da rawar takawa ta fuskar sanar da hukumomin abunda ya kamata ace sun mayar da hankali akai, baya ga batun taimakawa wajen isar da koken talakawa ga mahukunta dama sauran batutuwa da yan jarida zasu iya zama gatan mara gata.

Da yake gabatar da wata makala mai taken ‘’kariya da kuma tsaron dan jarida’’ shugaban jami’ar Kashere dake jihar Gombe Farfesa Umar Pate ya bukaci yan jaridu da suka ringa lura da sha’anin lafiyar farko kafin komai a aikin jaridar.

Karshe a nasa jawabin mawallafin jaridar Solacebase Abdullatef Abubakar Jos, yace sun shirya bayar da horon ga yan jaridu ne domin jawo hankali su zuwa ga yin rahotanni da suka shafi bangaren lafiya, da kuma bincikar yadda ake kasha makudan kudaden da akan ware domin kula da lafiyar al’umma.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...

Mun gano yadda yan Bauchi ke mamaye dazukan Kano – Gwamnatin Kano

Daga Nazifi Dukawa     Gwamnatin jihar Kano ta ce ta gano...