Matar wanda a ke zargi da kashe Hanifa ta bada shaida a kansa a kotu

Date:

 

A jiya Alhamis ne Jamila Sani, matar Abdulmalik Tanko, wanda a ke zargi da yin garkuwa da kuma kashe Hanifa Abubakar, ƴar shekara 5 a Jihar Kano, ta bada shaida a kan mijinta.

Tun a zaman kotun na jiha ne lauyan gwamnati, Musa A. Lawal ya gabatar da shaidu guda uku bayan da a zaman kotun na baya Tanko ya nisanta duk tuhume-tuhumen da a ke masa.

Shaidun sun haɗa jami’an ƴan sandan farin kaya, DSS biyu sai kuma ɗan sanda guda daya, wanda shi ne ma wanda ya binciki laifin.

Da a ke mata tambayoyi a zaman kotun na jiya, matar Tanko ta tabbatar da cewa ya kawo Hanifa gidan, inda ba ta fi tsawon kwanaki shida ba.

A cewar matar, da ta tambayi Tanko ko ƴar waye sai ya ce ai ƴar malamar da ke aiki a makarantar sa ne, inda ya ce mahaifiyarta ta samu aiki a Saudi Arebiya shi ne ta tafi Abuja domin cike wasu takardu.

Matar Tanko ɗin ta ƙara da cewa da wasa da wasa sai da Hanifa ta kwana shida a gidan su, sannan da daddare wajen ƙarfe 11 na dare ya ɗauke ta da ga gidan.

Da a ka nuna mata hoton Hanifa, matar Tanko ta tabbatar da cewa ita ce yarinyar da mijin nata ya kawo har ta yi kwanaki 6, har ma ta saba da ƴaƴan ta a gidan.

“Ban san cewa Hanifa ta mutu ba sai da jami’an DSS su ka zo gidan mu, sannan na san halin da a ke ciki,” in ji matar Tanko.

Kadaura24 ta rawaito cewa kawo yanzu dai, an gabatar da shaidu guda takwas a kotun.

Alƙalin kotun, Usman Na-abba, ya umarci a maida waɗanda a ke zargi gidan yari har sai ranar 9 da 10 ga watan Maris za a ci gaba da shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...

Al’ummar Kano ku baiwa AA Zaura hadin Kai domin ya kawo karshen fadan Daba – Baba Yawale

Daga Halima Umar Dogo   Babban Hadimin AA Zaura Alhaji Baba...

Gwamnatin Kano ta magantu kan Hukuncin kotu na zaben kananan hukumomi

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Kano ta bayyana farin...