Karancin mai: Kamfanin NNPC ya fara lodin man fetur ga gidajen mai don magance matsalar

Date:

Daga Maryam adamu baba
 Kamfanin kula da albarkatun man fetur na kasa NNPC, ya fara lodawa manyan motoci man don rabawa ga kowanne gidajen mai domin magance karancin man da ake fama da shi a fadin kasar nan.
 Manajan Daraktan Rukunin Kamfanin na NNPC, Mele Kyari ne ya bayyana haka ga manema labarai a Abuja ranar Laraba jim kadan bayan kammala wani taro da Kungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Gas ta Kasa, NUPENG, da Kungiyar Direbobin Tankar Man Fetur ta kasa, PTD.
 Mele Kyari ya ce raba man fetur din zai kawo saukin matsanancin halin da al’umma suke ciki Saboda dogayen layukan da ake ci gaba da samu a manyan buranan kasar nan.
 “A halin yanzu, muna da sama da lita biliyan 1.7 na man fetur a hannunmu”. Inji Kyari
 “Wannan yana nufin cewa a yanzu muna da ikon yin lodi fiye da kima daga dukkan wuraren ajiyarmu.  Mun dauki gabarar tabbatar da yin lodin man sa’o’i 24 a duk wuraren ajiyar da muke dasu”.
 “Wannan zai tabbatar da magance  karancin man da Kuma wahalhalun da Yan Ƙasar nan suka fuskanta.
Shugaban Kamfanin na NNPC ya nemi afuwar ‘yan Najeriya kan radadin da suka fuskanta a gidajen mai, ya kuma yi kira ga masu amfani da su da su guji sayar da man fiye da Farashin da gwamnati ta kaiyade.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...