Da dumi-dumi: APC ta Amince Shugaban Jam’iyyar ya fito daga Shiyyar Arewa

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida
 Jam’iyyar APC mai mulkin Nigeria ta tsayar da Amince ta fitar da shugabanta daga yankin Arewacin Najeriya a Babban zaben da zata gudanar.
 Gwamna Nasiru El-Rufai na Kaduna da Atiku Bagudu na Kebbi, ne suka bayyana hakan a lokacin taron manema labarai da suka gudanar bayan ganawar da shugaban kasa Muhammadu Buhari a Abuja.
 El-Rufai ya ce jam’iyyar ta amince da sauya mukaman Shugabannin jam’iyyar Musamman na kwamitin kolin jam’iyyar na kasa (NWC) tsakanin Arewa da Kudancin kasar nan a babban taron jam’iyyar wanda za ta gudanar a ranar 26 ga Maris 2022.
 Idan dai za a iya cewa, mukamin shugaban jam’iyyar na kasa wanda tsohon Gwamna John Odigie-Oyegun da Adams Oshiomhole na Jihar Edo Suka rike sun fito ne daga Kudu to shi ne zai koma Arewa.
 El-Rufai ya ce, “Mun amince da tsarin shiyya-shiyya na shiyyoyin siyasa guda shida, kuma mun yi musanya da su. Shiyyoyin Arewa za su dauki mukaman da shiyyar Kudu Suka rike shekaru takwas da suka wuce.
 “Don haka, tsari ne mai sauqi qwarai, daidaito da adalci.  Yanzu za mu koma mu tuntuba a matakin shiyya, mu duba mukaman da ake da su kuma za a fara shirye-shiryen taron da ka’in da na’in.  Don haka da yardar Allah ranar 26 ga Maris za mu yi babban taron mu na kasa.”inji El-Rufa’i
  taron dai ya gudana ne a zauren majalisar zartarwa ta Kasa dake fadar shugaban kasa a Abuja ya samu halartar mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo da gwamnoni 19 da suka hada da na Yobe, Kano, Kogi, Ekiti, Nasarawa, Kwara, Ebonyi, Jigawa, Lagos, Imo.  Ogun, Borno, Niger, Gombe, Osun, Kebbi, Plateau, da kuma mataimakin gwamnan jihar Anambra wanda ya baro jam’iyyar APGA zuwa APC a bara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...