Bayan Hukuncin kotu, Ganduje ya yi zazzafan Maratani ga yan G7

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya mayar da zazzafan martani ga tsagin su Malam Ibrahim Shekarau biyo bayan hukuncin da Kotun ɗaukaka ƙara ta yanke akan rushe hukuncin da wata kotu a Abuja tayi na rushe Shugabancin APC a matakin mazaɓu da ƙananan hukumomi ɓangaren Ganduje.

Kadaura24 ta rawaito cewa bayan hukuncin da kotu ta yanke a safiyar wannan rana, gwamna Ganduje yace Banza 7 sun faɗi wan-war akan rashin bin ka’idojin jam’iyya da kuma amincewa da jagorancin sa.

Yan banza 7 abun da sukai Kamar Suka dusa ne da damuna ko kuma ginin da aka yi fandushonsa da toka Kuma ace za a dora Masa ginin bulo”inji Ganduje

Ganduje Wanda yayi Magana Cikin Wani faifen video da yake Jawabi ga Wasu Yan Majalisu da Sauran mukarraban Gwamnatin Jihar Kano ya godewa Shugaban Rika na Jam’iyyar APC Mai Mala Buni bisa kokarin Ganin ya sulhun su day yan G7.

Ganduje ya Kuma yabawa dukkanin yan Jam’iyyar APC na Kano da matasa maza da Mata bisa goyon bayan da Suke baiwa Gwamnati da APC a Jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...