Daga Sayyadi Abubakar Sadeeq
Kotun daukaka kara ta Abuja ta yi watsi da hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke na soke taron mazabun da kananan hukumomin jihar Kano.
Kotun daukaka kara ta ce karamar kotun ba ta da hurumin sauraron karar da tsagin su Sanata Malam Ibrahim Shekarau suka gabatar mata.
Har ila yau, ta ce shari’ar ba ta kafin zabe ba ce, al’amari ne na cikin gidan jam’iyyar APC, don haka shugabannin jam’iyyar APC ne su zasu warware matsalar.
Ƙarin abin da za a bi: