Ra’ayi: Duk Wani Dan Najeriya Yana cin Arzikin Gwamna Tambuwal Ne a Yanzu – Comr. Dahiru Mukhtar

Date:

Daga Mukhtar Dahiru

Sanannen matashin dan gwagwarmayar nan wanda yayi suna wajen tofa albarkacin bakin sa kan al’amurran yau da kullum dake faruwa a Najeriya, Comr. Dahiru Mukhtar, ya ce a halin yanzu duk wani dan Najeriya yana cin arzikin gwamna Rt. Hon. Aminu Waziri Tambuwal ne na jihar Sokoto.

Comr. Dahiru, ya bayyana hakan ne yau Lahadi a Sahihin shafin sa na facebook, inda yace “Duk wanda ya kwana ya tashi a Najeriya daga shekarar 2014 zuwa yau yana cin arzikin jarumtar gwamna Aminu Waziri Tambuwal.

Mukhtar Dahiru yace Tambuwal shi ne ya jagoranci ceto dimokuradiyyar Najeriya a lokacin da Jonathan ya danne ta zai yi mata yankan Kunkurun Bala”

Da yanzu ‘yan Najeriya mun zama bayi babu mai iya hawa Intanet ya bayyana ra’ayin sa”

“Wannan kawai ya ci mu sakawa (Matawallen Daular Usmaniyya) da kujerar shugabancin Najeriya 2023” Inji Comr. Dahiru Mukhtar

A makonni biyu da suka gabata ne dai gwamna Tambuwal na jihar Sokoto, ya bayyana aniyar sa ta tsayawa takarar shugabancin Najeriya a zaben shekarar 2023 mai zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...