Mun rabawa Marayu 1500 kayan Sallah Don Suma su yi Sallah Cikin farin Ciki – Auwal Danlarabawa

Date:

Daga Fatima Mai fata

An bukaci da a cigaba da taimakawa rayuwar marayu tun kafin su fada cikin wani kangi na rayuwa.

Anyi Kira da al’umma dasu kasance cikin tsarin tallafawa marayu da masu rangwamen karfi duba ga yadda rayuwar su ke kasance a wannan lokaci sabida rashin kulawar da basa samu.

Shugaban gidauniyar tallafawa mabukata daga tushe ( Grassroot Care & Aid Foundation) Amb. Auwal Muhd Danlarabawa ne ya bayyana hakan a lokacin da suke raba kayan sallah ga marayu da masu rangwamen gata guda1500 a wannan wata na Ramadan.

Yace gidauniyar ta dauki shekaru 10 tana gudanar da wannan tallafi na kayan abinci da kayan sallah ga marayun da gidauniyar ke dasu karkashin gidauniyar Wanda ake bawa marayun karatu kyauta a makarantun da gidauniyar ke dasu a kananan hukumomin nassarawa da Ungogo a jihar Kano.

Danlarabawa ya Kara da cewa a wannan wata suna raba abincin ciyarwa na mutane 12000 da kuma raba danyen abinci na mutane 3000 duk a wannan wata na Ramadan

Ambassador Auwal Muhd Danlarabawa ya Kara Kira ga al’umma dasu cigaba da taimakawa rayuwar marayu a kowanne lokaci a kowacce unguwa Dan samun ladan da Allah ya tanadar ga masu tallafawa mabukata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...