Mun rabawa Marayu 1500 kayan Sallah Don Suma su yi Sallah Cikin farin Ciki – Auwal Danlarabawa

Date:

Daga Fatima Mai fata

An bukaci da a cigaba da taimakawa rayuwar marayu tun kafin su fada cikin wani kangi na rayuwa.

Anyi Kira da al’umma dasu kasance cikin tsarin tallafawa marayu da masu rangwamen karfi duba ga yadda rayuwar su ke kasance a wannan lokaci sabida rashin kulawar da basa samu.

Shugaban gidauniyar tallafawa mabukata daga tushe ( Grassroot Care & Aid Foundation) Amb. Auwal Muhd Danlarabawa ne ya bayyana hakan a lokacin da suke raba kayan sallah ga marayu da masu rangwamen gata guda1500 a wannan wata na Ramadan.

Yace gidauniyar ta dauki shekaru 10 tana gudanar da wannan tallafi na kayan abinci da kayan sallah ga marayun da gidauniyar ke dasu karkashin gidauniyar Wanda ake bawa marayun karatu kyauta a makarantun da gidauniyar ke dasu a kananan hukumomin nassarawa da Ungogo a jihar Kano.

Danlarabawa ya Kara da cewa a wannan wata suna raba abincin ciyarwa na mutane 12000 da kuma raba danyen abinci na mutane 3000 duk a wannan wata na Ramadan

Ambassador Auwal Muhd Danlarabawa ya Kara Kira ga al’umma dasu cigaba da taimakawa rayuwar marayu a kowanne lokaci a kowacce unguwa Dan samun ladan da Allah ya tanadar ga masu tallafawa mabukata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...