‘Yan Majalisar Dokokin Zamfara 18 Cikin 22 sun amince da tsige mataimakin gwamnan jihar

Date:

Majalisar Dokokin Jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya ta jefa uria’r amincewa da tsige Mataimakin Gwamnan Mahdi Aliyu Gusau daga kan muƙaminsa da gagarumin rinjaye.

Yayin wani zama a jiya Alhamis, ‘yan majalisa 18 cikin 22 ne suka amince da ɗaukar matakin yayin da ɗaya tak ya ki amincewa.

Haka nan, ‘yan majalisar sun nemi Alƙalin Alƙalai na Zamfara Mai Shari’a Kulu Aliyu ya kafa kwamatin da zai binciki Mahdi bisa zargin saɓa sashe na 190 da 193 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.

Dangantaka tsakanin mataimakin gwamnan da uban gidansa Gwamna Bello Muhammad Matawalle ta yi tsami tun lokacin ya gwamnan ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a bara amma Mahdi ya ci gaba da zama a PDP.

Honorabul Shamsudden Hassan Bosko, shi ne Shugaban Kwamitin yada Labarai na majalisar kuma ya shaida wa Haruna Shehu Tangaza yadda aka yi wannan zaman.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...