Rikicin APC: An fito daga zaman sulhun da ake yiwa Ganduje da su Shekarau

Date:

Daga Sadiya Muhammad Sabo

An kammal Zaman sulhun da ake yiwa bangaren Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da na tsagin su Sanata Malam Ibrahim Shekarau, Wanda aka gudanar a yau din nan Juma’a.

Kadaura24 ta rawaito an dai gudanar da zaman sulhun ne karkashin jagorancin Gwamnan Jihar Yobe Kuma Shugaban Kwamitin Rikon jam’iyyar APC na Kasa Mai Mala Buni, Wanda aka gudanar da zaman a gidan Gwamnatin jihar Yobe dake Abuja.

Zaman na yau dai ya Sami halartar Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje Wanda a baya ya tura wakilci domin Fara Zaman sulhun, Inda a wancan lokaci aka saurari korafin kowanne bangare gabanin Wannan Zama na yau.

Rahotannin sun tabbatar da cewa jam’iyyar APC na sun Gudanar da sulhun ne gabanin hukuncin kotun daukaka Kara ya fito domin a samar da dai-daito a jam’iyyar.

Zaman na yau dai bayan Gwamna Ganduje akwai Sanata Malam Ibrahim Shekarau da Sanata Barau Jibril da Sanata Kabiru Ibrahim Gaya, sai Kuma Shugaban Masu Rinjayen na Majalisar wakilai Hon Alhassan Ado Doguwa da sha’aban Ibrahim Sharada da dai Sauran Masu Ruwa da tsaki a kowanne bangare.

Wasu rahotanni da Kadaura24 ta samu ta karkashin Kasa sun nuna bayan tsahon lokaci da aka bata ana tattaunawar daga karshe dai ba wata matsaya da aka cimma har yanzu.

Wasu dai Suna ganin hukuncin kotun daukaka Kara ne kawai zai iya raba wannna gardamar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...