Rikicin APC: An fito daga zaman sulhun da ake yiwa Ganduje da su Shekarau

Date:

Daga Sadiya Muhammad Sabo

An kammal Zaman sulhun da ake yiwa bangaren Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da na tsagin su Sanata Malam Ibrahim Shekarau, Wanda aka gudanar a yau din nan Juma’a.

Kadaura24 ta rawaito an dai gudanar da zaman sulhun ne karkashin jagorancin Gwamnan Jihar Yobe Kuma Shugaban Kwamitin Rikon jam’iyyar APC na Kasa Mai Mala Buni, Wanda aka gudanar da zaman a gidan Gwamnatin jihar Yobe dake Abuja.

Zaman na yau dai ya Sami halartar Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje Wanda a baya ya tura wakilci domin Fara Zaman sulhun, Inda a wancan lokaci aka saurari korafin kowanne bangare gabanin Wannan Zama na yau.

Rahotannin sun tabbatar da cewa jam’iyyar APC na sun Gudanar da sulhun ne gabanin hukuncin kotun daukaka Kara ya fito domin a samar da dai-daito a jam’iyyar.

Zaman na yau dai bayan Gwamna Ganduje akwai Sanata Malam Ibrahim Shekarau da Sanata Barau Jibril da Sanata Kabiru Ibrahim Gaya, sai Kuma Shugaban Masu Rinjayen na Majalisar wakilai Hon Alhassan Ado Doguwa da sha’aban Ibrahim Sharada da dai Sauran Masu Ruwa da tsaki a kowanne bangare.

Wasu rahotanni da Kadaura24 ta samu ta karkashin Kasa sun nuna bayan tsahon lokaci da aka bata ana tattaunawar daga karshe dai ba wata matsaya da aka cimma har yanzu.

Wasu dai Suna ganin hukuncin kotun daukaka Kara ne kawai zai iya raba wannna gardamar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...