Buhari Ya Amince Da kafa Kwamitin Bincike a Kan Hadiza Bala Usman

Date:

Daga Safiyya Abbas


 Shugaba Buhari ya amince da shawarar da Ma’aikatar Sufuri a karkashin Rotimi Amaechi ta bayar na kafa kwamitin bincike da zai binciki yadda ake gudanar da Hukumar Kula da Tashar Jiragen Ruwa ta Najeriya (NPA).


 Shugaban kasar a cikin wata sanarwa da ya fitar ta hannun babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai da yada labarai, Garba Shehu, ya kuma amince da cewa Manajan Darakta, Hadiza Bala Usman ta koma gefe yayin da ake gudanar da bincike, sannan Mohammed Koko zai rike mukamin a Matsayin Mai rukon kwaryar .


 Daraktan, Ma’aikatar Kula da zirga-zirgar jiragen Ruwa ne zai jagoranci kwamitin yayin da Mataimakin Daraktan Harkokin Shari’a na ma’aikatar shi zai  zama Sakatare.


 Sanarwar tace Minista Rotimi Shi Zai sanar da Sauran mambobin kwamitin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...

RMK@69: Kwankwaso Jagora Ne Mai Hangen Nesa, Abba Kuma Na Kawo Ci Gaba a Kano – Bakwana

Wani jigo a kungiyar Kwankwasiyya, kuma tsohon mai ba...

Da dumi-dumi: Tinubu ya nada sabon Minista

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya aike da sunan...