Kotu ta ba da umarnin kamo jarumi Sadiq Sani Sadiq

Date:

Daga Jamilu Bala

Kotun shari’ar Musulunci da ke Hotoro Masallacin Juma’a ta bayar da umarnin da a kamo mata Jarumin wasan Hausan Sadiq Sani Sadiq.

Wani mai shirya fina-finai Aliyu Muhammad Hannas, ne ya shigar dakarar a gaban kotun kan cewar ya baiwa jarumin kudi domin yayi masa aikin film, amma yaki zuwa don yin aikin, Inda yace hakan ya ja masa asara mai yawa.

Jarumi Sadiq Sani Sadiq

Alkalin Kotun Maishari’a Sagiru Adamu, yace Sadiq ya bijirewa Umarnin Kotu duk da sammacin da aka bashi, tare da like masa sammacin a jikinm gidansa amma yaki halartar zaman kotun.

 

Zuwa yanzu dai kotun ta baiwa Dan sandan Kotun umarnin kamoshi, duk inda yake zuwa gaban kotun.

Express Radio ta rawaito Kotun tace da zarar an kamo Jarumin wasan hausan Sadiq Sani Sadiq, za a cigaba da zaman sauraren shari’ar.

2 COMMENTS

  1. Its like you learn my thoughts! You appear to understand a lot about
    this, such as you wrote the guide in it or something.

    I think that you just could do with some p.c. to pressure the
    message home a little bit, but instead of that, that is great blog.
    An excellent read. I’ll definitely be back.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...