Chidari Ya sha Alwashin Sasanta Yan adaidaita da Hukumar Karota don Kawo karshen Yajin Aikin

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Alhaji Hamisu Ibrahim Chidari ya yi kira ga masu sana’ar babura masu kafa uku na adaidaita sahu da su dakatar da yajin aikin da suke yi domin ci gaban jihar.

Alhaji Hamisu Ibrahim Chidari ya yi wannan kiran a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.

Ya bayyana cewa, majalisar dokokin jihar Kano ta tuntubi hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Kano (KAROTA), da kuma shugabannin kungiyar masu tuka babur don sasanta rikicin cikin ruwan sanyi.

Ya kara da cewa, za a zauna domin tattaunawa tsakanin bangarorin biyu domin warware rikicin.

Alhaji Hamisu Ibrahim Chidari ya koka kan wahalar da fasinjoji ke fuskanta sakamakon yajin aikin da ya gurgunta al’amura a jihar kano.

Shugaban majalisar ya jaddada kudirin majalisar na ciyar da jihar gaba ta hanyar samar da dokoki da nufin inganta rayuwar jama’a.

Rediyon Najeriya ta rawaito cewa, yajin aikin da masu adaidaita sahu suka shiga a Kano ya jefa fasinjoji cikin mawuyacin hali sakamakon karancin ababen hawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...