Wasu ‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Mahaifiyar wani Dan Majalisa a Kano

Date:

Daga Maryam Muhd Zawaciki
Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da mahaifiyar Isiyaku Ali Danja, shugaban marasa rinjaye a majalisar dokokin jihar Kano da tsakar daren ranar Talatar data gabata.
 Majiyoyi sun ce maharan sun shiga gidan Hajiya Zainab da ke karamar hukumar Gezawa da misalin karfe 1:00 na dare dauke da makamai, inda suka tilasta mata fita daga dakinta suka kuma tafi da ita.
 Dan majalisar, Isyaku Ali Danja ya tabbatar da sace mahaifiyar tasa ga ‘yan jarida a ranar Laraba, yana mai  cewa har yanzu wadanda suka yi garkuwa da ita ba su tuntubesu  ba.
Jaridar Time Express ta rawaito Isiyaku Ali Danja, shi ne tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Kano kuma wakilin Gezawa a majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...