Wasu ‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Mahaifiyar wani Dan Majalisa a Kano

Date:

Daga Maryam Muhd Zawaciki
Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da mahaifiyar Isiyaku Ali Danja, shugaban marasa rinjaye a majalisar dokokin jihar Kano da tsakar daren ranar Talatar data gabata.
 Majiyoyi sun ce maharan sun shiga gidan Hajiya Zainab da ke karamar hukumar Gezawa da misalin karfe 1:00 na dare dauke da makamai, inda suka tilasta mata fita daga dakinta suka kuma tafi da ita.
 Dan majalisar, Isyaku Ali Danja ya tabbatar da sace mahaifiyar tasa ga ‘yan jarida a ranar Laraba, yana mai  cewa har yanzu wadanda suka yi garkuwa da ita ba su tuntubesu  ba.
Jaridar Time Express ta rawaito Isiyaku Ali Danja, shi ne tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Kano kuma wakilin Gezawa a majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...