Wasu ‘Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Mahaifiyar wani Dan Majalisa a Kano

Date:

Daga Maryam Muhd Zawaciki
Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da mahaifiyar Isiyaku Ali Danja, shugaban marasa rinjaye a majalisar dokokin jihar Kano da tsakar daren ranar Talatar data gabata.
 Majiyoyi sun ce maharan sun shiga gidan Hajiya Zainab da ke karamar hukumar Gezawa da misalin karfe 1:00 na dare dauke da makamai, inda suka tilasta mata fita daga dakinta suka kuma tafi da ita.
 Dan majalisar, Isyaku Ali Danja ya tabbatar da sace mahaifiyar tasa ga ‘yan jarida a ranar Laraba, yana mai  cewa har yanzu wadanda suka yi garkuwa da ita ba su tuntubesu  ba.
Jaridar Time Express ta rawaito Isiyaku Ali Danja, shi ne tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Kano kuma wakilin Gezawa a majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...