Bana Nadamar Goyon Bayan Ganduje da nayi har ya Zama Gwamna – Kwankwaso

Date:

Daga Zainab Muhd Darmanawa
 Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabi’u Kwankwaso, ya ce ba ya nadamar goyon bayan Gwamna Abdullahi Ganduje har ya zama Gwamnan jihar kano.
 A lokacin da Sanata Kwankwaso yake tattaunawa da gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi, ya yi jawabi game da dangantakarsa da Gwamna Ganduje a baya, da kuma yadda suka yi aiki tare har zuwa 2015.
 “Ba ni da wani nadama ko kadan saboda har yanzu muna da karfi, mun fi 2015 karfi. Ba wai a Kano kadai ba har ma a fadin kasar nan da ma wajen,” in ji shi.
 An fara zaben Kwankwaso a matsayin gwamnan jihar kano a shekarar 1999 kuma an sake zabersu a shekarar 2011, inda ya cika shekaru takwas da yana mulkin jihar kamar yadda kundin tsarin mulki ya ba shi dama.
 Lokacin da Ganduje ya zama gwamna, Kwankwaso a lokacin Sanata ne mai wakiltar Kano ta tsakiya a shekarar 2015.
 Duk da cewa an zabe shi a jam’iyyar PDP, mataimakinsa na lokacin, Abdullahi Ganduje, ya gaje shi a 2015 a matsayin dan takarar jam’iyyar APC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...