Bana Nadamar Goyon Bayan Ganduje da nayi har ya Zama Gwamna – Kwankwaso

Date:

Daga Zainab Muhd Darmanawa
 Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabi’u Kwankwaso, ya ce ba ya nadamar goyon bayan Gwamna Abdullahi Ganduje har ya zama Gwamnan jihar kano.
 A lokacin da Sanata Kwankwaso yake tattaunawa da gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi, ya yi jawabi game da dangantakarsa da Gwamna Ganduje a baya, da kuma yadda suka yi aiki tare har zuwa 2015.
 “Ba ni da wani nadama ko kadan saboda har yanzu muna da karfi, mun fi 2015 karfi. Ba wai a Kano kadai ba har ma a fadin kasar nan da ma wajen,” in ji shi.
 An fara zaben Kwankwaso a matsayin gwamnan jihar kano a shekarar 1999 kuma an sake zabersu a shekarar 2011, inda ya cika shekaru takwas da yana mulkin jihar kamar yadda kundin tsarin mulki ya ba shi dama.
 Lokacin da Ganduje ya zama gwamna, Kwankwaso a lokacin Sanata ne mai wakiltar Kano ta tsakiya a shekarar 2015.
 Duk da cewa an zabe shi a jam’iyyar PDP, mataimakinsa na lokacin, Abdullahi Ganduje, ya gaje shi a 2015 a matsayin dan takarar jam’iyyar APC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...